INEC Ta Fitar Da Ranakun Zabukan 2023

Hukumar Zabe ta Kasa Mai Zaman Kanta (INEC) ta sanar da ranakun da za a gudanar da zabukan shekara ta 2023 masu zuwa.

Shugaban Hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu ne ya sanar da hakan a Abuja lokacin yake yi wa ’yan jarida jawabi.

A cewarsa, za a gudanar da zaben Shugaban Kasa da na ’yan majalisar tarayya ranar 25 ga watan Fabrairun 2023, yayin da za a gudanar da zaben Gwamnoni da na ’yan majalisun jihohi ranar 11 ga watan Maris na shekarar.

Farfesa Mahmud ya ce, “Za a yi zaben Shugaban Kasa da na ’yan majalisar tarayya ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.

“Na Gwamnoni da ’yan majalisun jihohi ranar 11 ga watan Maris din 2023. Daga yau [Asabar] ke nan, saura kwana 365 babban zaben 2023,” inji Farfesa Mahmud.

Shugaban na INEC ya kuma ce za a fara yakin neman zaben Shugaban Kasa daga ranar Laraba, 28 ga watan Satumban 2022, sai kuma na Gwamnoni da za a fara daga 12 ga watan Oktoban 2022.

Hukumar ta kuma ce za a kammala yakin neman zaben Shugaban Kasa ranar 23 ga watan Fabrairun 2023, sai kuma na Gwamnoni ranar tara ga watan Maris din 2023.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Back to top button