An Sanya Ranar Fara Rijistar UTME/JAMB Ta Shekarar 2022
![An Sanya Ranar Fara Rijistar UTME/JAMB Ta Shekarar 2022 An Sanya Ranar Fara Rijistar UTMEJAMB Ta Shekarar 2022](/wp-content/uploads/2022/01/An-Sanya-Ranar-Fara-Rijistar-UTMEJAMB-Ta-Shekarar-2022.jpg)
Hukumar shirya jarrabawar JAMB (Joint Admission and Matriculation Board) ta Sanya ranar fara rijistar jarrabawar JAMB na shekarar 2022/2023
Bayan daukar lokaci da hukumar tana tattaunawa da duba lokacin da ya dace, hukumar ta sanya ranar 18th February 2022 yazamo ranar da zaa fara registration na UTME a duka fadin kasa. Hukumar ta kuma tabbatar da cewar zaa fara zaman wannan jarrabar a ranar 17th April 2022 a duka santoci da hukumar ta tabbatar tareda tantancewa wato Jamb accredited centers.
Wannan sanarwa ta fito ne daga bakin shugaban hukumar ta Jamb professor Ishaq Olayede a Abuja. Shugaban ya kara da cewar Jarrabawar da zaa zauna ta shekarar 2022/2023 zaa sayarda itane kamar yadda aka saba a official portal na hukumar www.jamb.gov.ng a ranar 18th February 2022 ga dukkan daliban da keda shirin shiga jami’a ko sauran makarantun gaba da secondary.