Education

NECO Ta Kara Wa’adin Fara Jarabawa

Sponsored Links

Hukumar shirya jarabawar kammala sakandare ta NECO ta kara wa’adin rajistar jarabawar zuwa 12 na daren 20 ga watan Yuni, 2022.

Shugaban Sashen Yada Labaran hukumar, Azeez Sani ne ga bayyana hakan, in da ya ce a baya hukumar ta ware ranar 30 ga watan Mayu a matsayin ranar rufewa.

Haka zalika Sani ya ce an shirya fara jarabawar daga ranar 27 ga watan Yuni zuwa 12 ga watan Agusta, kuma darussa 76 za a yi jarabawar kansu.

Haka kuma ya ce babu wani wa’adi da a yanzu hukumar za ta kara, tare da yin kira ga ma’aikatun ilimi da shugabnnin makarantun sakandare, da sauran masu ruwa da tsaki da su yi amfani da wannan dage jarabawar ta hanyar da ta dace.

hausadrop

Aminu B Yusuf, Editor in Chief at HausaDrop.Com

Leave a Reply

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Back to top button