Yadda ’Yan Bindiga Suka Sa Garin Kaduna A Tsakiya

’Yan bindiga sun sa garin Kaduna a tsakiya, lamarin da ya haddasa karuwar ayyukan garkuwa da mutane a garuruwa da kauyukan da ke kusa da garin.
Daruruwan mutane da suka kaurace wa gidajensu a yankunan a wajen garin Kaduna saboda ayyukan ’yan bindiga suka dawo kusa da garin Kaduna sun shaida mana cewa ’yan bindigar na ci gaba da bibiyar su a inda suka dawo.
A baya-bayan nan ’yan bindiga sun yawaita kai hare-hare a gidaje da kauyukan da ke kusa da garin Kaduna, wanda ya sa ake fargabar cewa tsaurin idonsu na kara karuwa.
Sai dai wasu majiyoyin tsaro sun shaida mana cewa rikicewa ’yan bindigar suka yi saboda uzzura musu da jami’an tsaro suka yi da hare-hare a maboyarsu da ke cikin daji, shi ya sa suka koma kai hari a cikin al’ummomi da ke kusa da garin Kaduna, domin guje wa shiga hannun jami’an tsaro.
Yanzu dai kusan shekara 10 ke nan da ayyukan ’yan bindiga ya fara raba mutane da dama da muhallansu a yankin Kaduna ta Tsakiya.
Tun a shekarar 2013, Sarkin Birnin Gwari, Alhaji Zubairu Jibril Mai Gwari, ya bayyana kokensa game da ayyukan ’yan bindga da ke mamaye wasu yankuna da ke karkashin masarautarsa.
Daga baya ayyukan bata-garin suka rika watsuwa zuwa Kananan Hukumomin Chikun, Igabi, Giwa da kuma Zariya, a baya-bayan nan.
A bisa binciken da muka gudanar a makonnin baya-bayan nan, mun gano cewa a ’yan watannin nan, an samu karuwar aikata miyagun laifuka a yankin Birnin Kaduna, musamman a birnin Zariya, da kuma garuruwan Birnin Gwari da Giwa.
A baya wadannan yankuna su ne suka kasance mafaka ga mutanen da suka gudo daga yankunansu saboda yadda ’yan bindiga suka fitine su.
Source: Aminiya Dailytrust