Buhari Ya Rattaba Hannu A Kan Kudurin Dokar Zabe

Advertisement
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya rattaba hannu a kan kudurin Dokar Zabe na 2021 da aka dade ana takaddama a kansa.
Buhari ya sanya hannu a kan kudurin ne da misalin karfe 12:25 na ranar Juma’a.
Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan da Shugaban Majalisar Wakilai Femi Gbajabiamila da wasu ‘yan majalisa ne suka shaida sa-hannun.
Shugaban Majalisar Dattawan ya ce dokar da aka sanyawa hannu ta zo da gagarumin ci gaba domin za ta samar da gaskiya ga tsarin zabe.
Sai dai shugaba Buhari ya bukaci Majalisar Dokokin Najeriya ta sake yin aiki don haramta wa masu rike da mukaman siyasa shiga takara, har sai sun cika ka’idojin kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya.
Cikakken bayani ma tafe…