Wutar Lantarki Ta Babbake Barawon Wayar Transfoma

Wutar lantarki ta babbake wani mutum har lahira a lokacin da yake kokarin sace wayar wutar transfoma a kauyen Lambu da ke Karamar Hukumar Tofa ta Jihar Kano.

Wani mazaunin garin mai suna Naziru Lambu ya ce abin ya faru ne da misalin karfe 1 na dare kafin wayewar garin Laraba.

Ya bayyana cewa wutar ta babbake mutumin ne bayan da ya gama kwance wayoyin har ya ajiye su a kusa da tranfomar.

Ya ce wasun ’yan garin sun ce sun ji karar tartsatsin wutar lantarki a cikin dare da kuma ihun mutumin da ake kyautata zaton barawo ne kafin ya mutu.Ya ce an tsinci gawar mutumin tana lilo, shi kuma ya rike waya a hannunsa.

Tuni dai jami’an tsaro da na kamfanin wutar lantarki ta KEDCO suka isa kauyen Lambu domin gudanar da bincike a kan abin da ya faru.

Source: Aminiya Dailytrust

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Back to top button