Zuwan A’isha Buhari Kano Bayan Ta’aziyya Ta Nemi Ayiwa Wanda Ya Kashe Hanifa Hukunci

Daga: Fahad Kabir Mai Tata
Mai dakin shugaban Najeriya, Aisha Buhari ta ziyarci Kano domin ta’aziyya ga iyalan Sheik Ahmad Bamba da kuma Hanifa Abubakar, yarinyar nan ‘yar shekara biyar da mai kamarantarsu ya kashe ta.
A jawabin da ta gabatar a gidan gwamnatin jihar Kano a ranar Laraba, Aisha Buhari ta ce ta je jihar ne a ziyararta ta kashin-kanta domin jajanta wa gwamnan Kano da matarsa, da Sarkin Kano da kuma al’ummar jihar a kan rasuwar Sheikh Ahmad Muhammad Ibrahim Bamba da kuma Hanifa Abubakar.
Game da kisan da aka yi wa Hanifa, matar shugaban kasar ta ce tana fata tare da addu’ar fatan za a yi wa yarinyar adalci.
Ta ce: ‘’A matsayina na uwa ina da ‘ya’ya da jikoki wadanda tuni suna makarantar firamare. Sun amince da malamansu sosai haka mu ma kuma.
Saboda haka a yanayin da za a ce ‘ya’yanmu ba su tsira ba a makarantunsu, to lalle hakan na nuna ba shakka al’umma ta zama wani abu daban. Ina ganin ya kamata a yi hukuncin domin kwantar da hankula a Najeriya.’’
Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ba wa Aisha Buhari tabbacin cewa lalle za a tabbatar an yi adalci a kan kisan na Hanifa, wadda ya ce, ‘’Hanifa ‘yarmu ce kuma ‘yar ‘yan Najeriya ce,’’
Mai dakin shugaban Najeriyar ta kai ziyarar ta’aziyya gidan su Hanifa, inda ta yi wa iyayen yarinyar, wadda kisanta ya dauki hankali a Najeriya, ta’aziyya.