Yanzu APC Na Da Mambobi Miliyan 40 A Najeriya – Buni

Shugaban kwamitin riko na jam’iyyar APC na kasa kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce yanzu haka jam’iyyarsu na da mambobi akalla miliyan 40 a Najeriya.

Ya ce sun tattara alkaluman ne bayan kammala aikin sake rajistan mambobin jam’iyyar da aka gudanar a kwanakin baya.

Kazalika, Gwamnan ya kuma sanar da 26 ga watan Fabrairun 2022 a matsayin ranar babban taron jam’iyyar.

Ya sanar da haka ne ranar Talata, yayin taron mata na jam’iyyar da ke gudana a Abuja.

Gwamnan ya yi kira ga matan da su fito kwansu da kwarkwata a fafata da su a babban taron da ke tafe ta hanyar tsayawa takara.

Mai Mala ya kuma ce jam’iyyarsu a shirye take tsaf ta lashe babban zaben kakar 2023 da ke tafe.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Back to top button