Kashi 90 Cikin 100 Na Gwamnoni Ba Su Cancanci Shugabanci Ba

Mai Magana da Yawun Kungiyar Dattawan Arewa (NEF), Dokta Hakeem Baba-Ahmed, ya ce kashi 90 cikin 100 na gwamnonin Najeriya ba su cancanci ko da samun kusanci da shugabanci ba.

Dokta Hakeem Baba-Ahmed ya kara da cewa a cikin kowadanne gwamnoni 10 a Najeriya, mutum tara, “Ba su da shiri, ba su da kwarewa kuma ba su cancanci shugabanci ba.”

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a Babban Taron Tattaunawa na Daily Trust na Shekara-shekara karo na 19 a Abuja, ranar Alhamis.

Baba-Ahmed ya ce a halin yanzu, mutanen da ba su dace ba ne suke jagorantar mutane suke musu karfa-karfa, su kuma mutanen suke ta neman samun sabbin shugabannin da suka dace, wanda shi ma bai wadatar ba.

Don haka ya yi kira da a sauya fasalin tsarin Najeriya, yana mai cewa, “Abin da ya kamata shi ne mu dora tsarin federaliyya da muke bi a kan gadon fida mu tambayi kanmu, ina matsalar take?

“Me ya hana a rage karfin shugabanci ko gudanar da shi, a sauya tsarin kasa, amma na san wannan batu ne da shugabannin yanzu suke yawan amfani da ita.

Source: Aminiya Dailytrust

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Back to top button