Gwamnan Jihar Kebbi Atiku Bagudu ya bawa kungiyar Izala gudunmawar Naira Miliyan 50M domin gina Jami’ar Musulinci a Jihar Jigawa

Advertisement

Gwamnan jihar Kebbi Sanata Atiku Bagudu ya bawa kungiyar Izala gudunmuwar Naira Miliyan 50 domin gina jami’ar musulunci a Jigawa.

Bayanin hakan ya fito ne daga shugaban JIBWIS na kasa Sheikh Bala Lau a Iokacinda sukeje yi masa godiya a fadar Gwamnati dake birnin Kebbi.

Ga cikakkiyar sanarwar kamar haka “Wakilan Izalah bisa jagorancin Shugaban kungiyar Jibwis Nigeria na kasa Imam Sheikh (Dr) Abdullahi Bala Lau, sun ziyarci gwamna Kebbi Sen, Abubakar Atiku Bagudu, a fadar gidan Gwamnati dake Birnin Kebbi.

A cewarjagoran tawagar Shugaba Imam Bala Iau, sun je gidan gwamnati ne domin nuna godiya ga gwamnan kan samun zaman Iafiya da ci gaban jihar tare da godewa gwamnan bisa samun tallafin Naira Miliyan Hamsin (N50,000,000.00) na tallafin da Gwamnatinsa ta basuwa domin gina Jami’ar As-Salam Global University Hadejia ajihar Jigawa.

Bugu da kari, ya sanar da Gwamnan jihar kan yadda aka warware rikicin da ke faruwa a cikin Shugabannin kungiyar na jihar Kebbi tare da gabatar da sabbin Shugabannin jihar.

A Iokacin da yake mayar da nashi jawabin, Mai Girma Gwamna Sen, Abubakar Atiku Bagudu, yayi godiya ga Shugabannin a ziyarar da suka kawo masa da Kuma yabawa Kungiyar ta JIBWIS na gudunmawa da kokarin da suke basuwa ga Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari, GCFR da kuma jiharsa (ta Kebbi).

Gwamnan ya kara godiya ga wakilan akan addua’arsu da goyon bayan da suke basuwa‘ Kuma ya gabatar musu da yara guda 30 da Malami Daya Wadanda aka karbo na FGC Yauri ya nemi da suyi musu addu’a.

Gwamna Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya jagoranci Sheikh Bala Lau da sauran Shugabannin Izala zuwa dakin taro na Banquet dake gidan gwamnati, inda suka gudanar da addu’o’i na musamman ga daliban da aka sako da kuma malamin kwalejin gwamnatin tarayya dake Birnin Yauri.

Shugaba Bala Iau bayan sun kammala ganawa da Daliban da da Malami Daya, da yi musu addu’a, ya yabawa Gwamnatin Jihar Kebbi (Kebbi State Government of Nigeria) na kokarin kubutar da wadannan Daliban.

Shugaba Sheikh Bala Iau, yayi matukar godiya da yabo ga Gwamna Sen, Abubakar Atiku Bagudu, cewa ya cika alkawalin da ya dauka na bada tallafin Miliyan Hamsin, ga Jami’ar As-Salam Global University Hadejia, A ranar da aka
kaddamar da ita.

Shugaban Izala ya bayar da shawarar gudanar da taron tuntubarjuna tsakanin Gwamnoni da malaman addini a Iokaci-Iokaci domin tuntuba tare da Ialubo hanyoyin magance kalubalen da ake fuskanta da suka shafi tsaro, tattalin arziki,
shugabanci da siyasa.

Daga cikin Tawagar akwai Sakataren Izalah na kasa Sheikh (Dr) Muhammad Kabir Haruna Gombe.

Ya gabatar da takardar yabawa da godiya daga Shugaban kungiyar Jibwis Nigeria Sheikh Abdullahi Bala Iau zuwa ga Gwamna Sen, Abubakar Atiku” Bagudu.

Daga cikin Tawagar Shugaba Bala Iau akwai: Sheikh Abubakar Giro Argungu, Sheikh Alaramma Ahmad Suleiman Ibrahim Kano da Sheikh Dr Ibrahim Jalo Jalingo sauransu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Back to top button