Ban Ji Dadin Sanya Hotona A Labarin Rikicin Kannywood Ba – Rahama Sadau

Ban Ji Daɗin Sanya Hotona A Labarin Rikicin Kannywood Ba, Cewar Rahama Sadau
Fitacciyar jaruma a masana’antar fina-finai ta Kannywood, Rahama Sadau, ta koka kan yadda aka sanya hotonta a labarin da aka wallafa kan yadda batun biyan ‘yan fim ya raba kan masana’antar.
Jarumar dai ta ce ba ta ji dadin yadda labarin da sashen Hausa ya wallafa a kan batun ya kunshi hotonta ba a labarin, wanda ya samo asali tun bayan hirar da shashen ya yi da Ladin Chima, daya daga cikin jaruman na Kannywood .
Jarumar ta bayyana hakan a ne a kafar sadarwa ta Twitter inda ta bayyana cewa ita ba tace komai ba a cikin wannan rikici amma kuma BBChausa sun sanya hotonta a cikin jerin wadanda rikicin ya shafa.
Jarumar dai ta sake wallafa labarin a Twitter tare da rubuta”To ni kuma mai ya kawo hotona ciki?, ko neman magana?” a jikin labarin.
Wannan ya sa mutane dake bibiyar shafin tofa albarkacin bakinsu a kai, inda wasu ke ganin kafar BBC ta yi amfani da hoton nata ne domin jan hankalin masu karatu.
Sai dai kuma a cikin labarin, BBC ta bayyana yadda jarumar da ma wasu daban irin su Adam Zango suka nuna nuna alamar yin shiru, duk da sun nuna akwai magana.